Buhari ya ziyarci Abuja tun bayan saukarsa daga mulki


A karon farko tun bayan da ya mika mulki ga Gwamnatin shugaba Tinubu Tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya ziyarci Abuja Babban birnin kasar a Talatar makon nan. 

Shugaban wanda ya halarci taron kaddamar da littafi wanda hadiminsa Femi Adesina ya wallafa dangane da yadda ya yi aiki tare da shugaba Buhari.

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu tare da wasu jiga-jigan gwamnatinsa da ma tsofaffin hadiman gwamnatin Buhari sun halarci taro wanda aka gudanar a otal din Transcorp da ke Abuja.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp