Atiku ya yi martani kan cefanar da matatar man Fatakwal


Tsohon ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya ce Anƙi zaɓarsa saboda zai sayar da NNPC yanzu gashi gwamnatin Tinubu zata siyar.

Atiku ya bayyana hakan a wani rubutu da ya wallafa a shafin sa na X.

Atiku dai ya mayar da martanin ne kan matakin da kamfanin na NNPC ya dauka na mika matatar mai ta Fatakwal ga wani kamfani mai zaman kansa domin ya cigaba da gudanar da aiki a cikin sa 

Ya bayyana cewa dole ne kamfanin man na NNPC ya bayyana wa ‘yan Najeriya abin da za su samu ta hanyar mika matatar ga kamfanin.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp