Kamfanin da ke aikin titin Abuja-Kano na son karin kudi N1.35tn, inji Minista

 

Hanya

Ministan ayyuka a Nijeriya Sen. David Umahi, ya ce kamfanin Julius Berger na neman karin Naira Tiriliyan N1.35tr domin kammala aikin hanyar Abuja-Kaduna-Kano.

Ministan ya bayyana hakan yayin da yake yi wa manyan Daraktocin ma'aikatar ayyukan jawabi a ranar Alhamis. 

Aikin dai na daya daga cikin ayyukan da gwamnatin Shugaba Tinubu ta gada daga tsohuwar gwamnatin shugaba Buhari.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp