Jerin jami'o'in da hukumar kula da jami'o'i ta kasa zata bincika



Hukumar kula da jami’o’I ta kasa ta lissafo jerin wasu jami’o’in cikin gida mallakar gwamnati da masu zaman kansu da zata fara bincike akan su sakamakon zargin su da bayar da shaidar kammala karatu ta bogi.

Duk dai wannan na zuwa ne bayan bankado asirin yadda wasu ‘yan Najeriya ke samo shaidar kammala jami’a cikin wata guda.

Ma’aikatar ilimi ta ce binciken farko-farko da ta gudanar ya gano yadda ake wannan badakala har a cikin gida, lamarin da ya sa dole ta magance wannan matsala, saboda inganta makomar kasar.

Jami’o’in sun hadar da:

1. National University of Nigeria, Keffi, jihar Nasarawa.

2. North Central University, Otukpo, jihar Benue.

3. Christ Alive Christian Seminary da jami’ar jihar Enugu.

3. Richmond Open University, Arochukwu, dake jihar Abia.

4. West Coast University, Umuahia.

5. Saint Clements University, Iyin Ekiti, a jihar Ekiti.

6. Volta University College, Aba, jihar Abia.

Illegal Satellite Campuses of Ambrose Alli University.

7. L. I.F.E Leadership University, Benin City,  jihar Edo.

 

 

 

 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp