Hukumar kula da jami’o’I ta kasa ta lissafo jerin
wasu jami’o’in cikin gida mallakar gwamnati da masu zaman kansu da zata fara
bincike akan su sakamakon zargin su da bayar da shaidar kammala karatu ta bogi.
Duk dai wannan na zuwa ne bayan bankado asirin yadda
wasu ‘yan Najeriya ke samo shaidar kammala jami’a cikin wata guda.
Ma’aikatar ilimi ta ce binciken farko-farko da ta
gudanar ya gano yadda ake wannan badakala har a cikin gida, lamarin da ya sa
dole ta magance wannan matsala, saboda inganta makomar kasar.
Jami’o’in sun hadar da:
1. National University of Nigeria, Keffi, jihar
Nasarawa.
2. North Central University, Otukpo, jihar Benue.
3. Christ Alive Christian Seminary da jami’ar jihar Enugu.
3. Richmond Open University, Arochukwu, dake jihar
Abia.
4. West Coast University, Umuahia.
5. Saint Clements University, Iyin Ekiti, a jihar Ekiti.
6. Volta University College, Aba, jihar Abia.
Illegal Satellite Campuses of Ambrose Alli
University.
7. L. I.F.E Leadership University, Benin City, jihar Edo.