Firaministan kasar Faransa Elisabeth Borne ta yi murabus daga mukaminta

Fadar Elysée ce ta kasar Faransar ta sanar da hakan inda ta ce Elisabeth din ta mika wannan takarda ce ta murabus din tata da ta gwamnatin ta baki daya a ranar jiya litinin din nan 8 ga Janairu ga shugaban kasar Emmanuel Macron 

A sakon da ya aike a shafinsa na X, shugaba Macron ya gode wa shugabar gwamnatin tasa mai barin gado dangane da aikin da ya ce ta yi ga kasar abin misali. Mrs Elisabeth dai da sauran membobin gwamnatin ta za su cigaba da wasu ayyukan yau da gobe har zuwa lokacin da za a nada sabuwar gwamnati.

Elisabeth Borne da aka nada a wannan mukami tun a watan Mayun 2022 ita ce mace ta biyu da ta rike wannan matsayi bayan Édith Cresson.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp