Da yiwuwar EFCC ta ci gaba da binciken Bello Matawalle kan batun kudin da suka Naira bilyan 70


Hukumar hana yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC ta ce a shirye take ta kakkabe batun nan da ke zargin tsohon Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle kan badakalar kudi Naira bilyan 70 a lokacin yana gwamna.

Da yake yi wa masu zanga-zanga bayani a hedikwatar hukumar, mukaddashin mai daraktan hulda da jama'a na hukumar Wilson Uwajaren, ya tabbatar musu da cewa za a yi adalci kan batun.

Da sanyin safiyar Juma'ar nan ne dai wasu mutane dauke da kwalaye karkashin kungiyar Zamfara Alternative Forum suka durfafi hedikwatar hukumar EFCC a Abuja inda suke neman hukumar da ta sake dawo da batun sabo kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Mr Uwajaren ya ce ba ma wannan batun ba, duk wani batu da ke gaban hukumar za a kakkabo shi, don tabbatar da an yi wa kowa adalci.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp