Nijar ta kulla yarjejeniyar tsaro da Rasha

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun rattaba hannu kan yarjejeniyar karfafa huldar tsaro da kasar Rasha.

A yayin wata ziyara ce da wata babbar tawagar kasar Rashar ta kawo Nijar ne karkashin jagorancin karamin ministan tsaron kasar manjo kanal Evkurouv Lunus-Bek aka kulla wannan wannan yarjejeniya tare da ministan tsaron Nijar janar Salifou Mody.

Daga bisani tawagar ta samu ganawa da shugaban gwamnatin mulkin sojan birgediya janar ABDOURAHAMANE Tiana a fadar sa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp