EFCC ta kama dan kwangilar ma'aikatar jin kai da Sadiya Umar Faruq ta jagoranta

Hukumar hana yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC ta ce ta kama dan kwangila James Okwete da hakan ke da nasaba da zargin wata badakalar kudi Naira bilyan 37 da ake zargin ministar jin kai a zamanin mulkin Buhari, Sadiya Umar Faruq.

Wani babban jami'in hukumar EFCC da ya sanar da jaridar Punch, ya ce dan kwangilar ya yi bayani gamsasshe a kan tsohuwar ministar da ma wasu tsoffin daraktoci a ma'aikatar.

Wannan batu dai ya zo daidai da lokacin da ake binciken wasu ministocin gwamnatin Buhari guda uku kan zargin wata badakalar kudin da aka kiyasta sun kai Naira milyan 150.

Majiyar daga hukumar EFCC ta ce da yiwuwar a kama Sadiya da sauran daraktocin da suka yi aiki a zamanin tana minista.

Yanzu haka dai bayanai sun ce ana tsare da dan kwangila Okwete a hedikwatar hukumar EFCC da ke Jabi, Abuja.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp