ECOWAS ta dorawa sojojin kasashen Nijar, Mali, da Burkina Faso alhakin karuwar ta'addanci a yammacin Africa


Kungiyar kasashen yammacin Africa ta ECOWAS ta zargi sojojin da suka yi juyin mulki a kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso a matsayin wadanda ke rura wutar ta’addanci a nahiyar


Shugaban majalisar gudanarwar kungiyar Omar Tourey ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi wajen bikin bude taron kungiyar kan tsaro da shiga tsakanin rikice-rikice karo na 51 da aka fara a Abuja.

Tourey ya ce juyin mulkin da sojojin suka yi, ya rusa duk wani tsari ko kokari da kungiyar ke yi na tabbatar da tsaro a yankin.

Ya kuma kara da cewa jan kafar da sojojin ke yi wajen mika mulki hannun farar hula na baiwa ‘yan ta’adda da masu daukar nauyin su kara azama wajen kaddamar da hare-hare kan fararen hula.


Tourey ya kuma nuna takaicin sa kan yadda sojojin ke amfani da juyin mulkin wajen yada farfaganda irin ta siyasa yayin da suke nunawa duniya cewa zaluntar su ake yi.


Kididdiga ta nuna cewa juyin mulkin da sojoji suka yi a wadannan kasashe ya jefa jama’a kusan miliyan 5 cikin yunwa da bakin talauci, sai wasu miliyan 2.5 da suka rasa muhallan su, inda ya tilasta rufe makarantu fiye da dubu 9.

 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp