Adadin wadanda suka mutu a sanadin harin sojoji a Kaduna ya karu zuwa 120-Amnesty international



Kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International ta ce adadin wadanda harin bam din sojoji ya kashe a kauyen Tungar biri na jihar Kaduna ya kai 120 zuwa yanzu.

Bayanai na nuna cewa har yanzu babu wani alamu a aikace na daukar mataki kan sojojin da suka aikata wannan danyen aiki, in banda Allah wadai da gwamnati ta yi.

Har ya zuwa yanzu dai akwai mutane fiye da 50 da ke kwance rai a hannun Allah a asibiti suna karbar kulawar jami’an lafiya bayan wannan abin takaici da ya rutsa da su.

Sai dai kuma adadin da Amnesty ta bayar ya ci karo da wanda hukumar bayar da agaji ta kasa NEMA ta bayar wanda ke cewa kawo yanzu mutane 85 ne suka mutu a sanadin harin, yayin da 66 suka jikkata.

Wannan dai ba shi ne karon farko da jami’an sojoji ke hallaka mutane da sunan kuskure a arewacin Najeriya ba, inda kididdiga ke nuna cewa ire-iren wadannan hare-hare sun kashe mutanen da basu ji ba basu gani ba har sama da 400 daga 2014 zuwa yanzu, musamman a jihohin Borno da Zamfara.

 

 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp