Duk kotun da za a je Gawuna ke da nasara - Ganduje

Shugaban jam’iyyar APC na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya yaba da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na tsige gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf tare da bayyana dan takarar jam’iyyar APC a zaben ranar 18 ga watan Maris Nasir Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben.

Ganduje ya ce APC za ta sake yin nasara idan jam’iyyar NNPP da Gwamna Yusuf suka garzaya kotun koli.

Da yake mayar da martani kan hukuncin yayin wani taron manema labarai a ranar Juma’a a Abuja, Ganduje ya ce gwamnatin Gawuna za ta samar da damammaki masu kyau ga talakawa tare da samun nasarori fiye da shekaru takwas da ya yi yana gwamnan jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp