'Yan Nijeriya sama da milyan 90 ba su samun hasken lantarki - Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya ce shekaru 10 bayan cefanar da sashen lantarki na kasar, har yanzu akwai mutane sama da milyan 90 da ba su samun lantarkin yadda ya kamata.

Da ya ke magana a Abuja, Shugaba Tinubu ya koka cewa babban layin lantarki na 'National Grid' na wadatar da kaso 15% kacal na al'ummar Nijeriya.

Ya ce hakan ke barin gidaje da masana'antu da dama su dogara da janaretoci da sauran hanyoyin samar da makamashi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp