Na fi Akpabio kwarewa da gogewa a aikin majalisa - Ndume

Sanata Ali Ndume mai tsawatarwa na majalisar dattawan Nijeriya, ya sanar cewa ya fi shugaban majalisar Sanata Godswill Akpabio gogewa da kwarewa a aikin majalisa.

Sanata Ndume da ke wakiltar Borno ta Kudu ya sanar da hakan ne a cikin wani shirin gidan talabijin na Channels, Abuja.

Tun dai a shekarar 2011, Sanata Ali Ndume ya ke majalisar dattawan, amma shi Akpabio ya fara zuwa majalisar dattawan ne a shekarar 2015.

Sanata Ndume dai ya sanar da dalilinsa na ficewa daga majalisar a lokacin da Akpabio ya katse shi lokacin da ya ke magana a majalisar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp