Atiku ya rubuta wa Hedikwatar BBC korafi bisa zargin bayar da labarin son zuciya kan ingancin takardun Tinubu


Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya rubuta wa Hedikwatar BBC takardar korafi bisa zargin wuce gona da iri kan ingancin takardun Shugaba Tinubu.

A cikin wani kundi, BBC ta yi bayani dalla-dalla kan ingancin karatun boko na Bola Ahmad Tinubu. Binciken BBC dai ya sanar cewa babu inda shugaba Tinubu ya yi karya a takardunsa.

Sai dai mai magana da yawun Atiku Abubakar, Phrank Shaaibu a hira da ya yi da gidan talabijin na Channels, ya ce binciken BBC cike yake da son zuciya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp