Rahotanni daga jihar Kaduna da ke Arewacin Nijeriya na cewa wasu 'yan bindiga sun kai hari a wani masallaci da ke kauyen Saya-Saya a karamar hukumar Ikara kamar yaddajaridarDailytrust taruwaito.
Majiyar ta DCLHausa ta ce a yayin harin 'yan bindigar sun kashe masallata 5.
Lamarin dai ya faru ne da misalin karfe 8 na dare na ranar Juma’a a daidai lokacin da mutanen ke gudanar da Sallar Isha’i a wannan masallaci.
Mansir Alhassan shi ne
mukaddashin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ya tabbatar da faruwar lamarin a Asabar din nan a Kaduna.