Tura ta kai bango: Dole mu yi yajin aiki - NLC

Kungiyar Kwadago a tarayyar Nijeriya NLC ta ce za ta fara wani yajin aikin gargadi na kwanaki biyu daga ranar Talata 5 ga wannan wata na Satumba.

NLC ta ce yajin aikin ya zame mata tilas domin ta nuna adawa da matakin gwamnatin kasar kan nuna gazawarta karara na kasa magance kalubalen da yan kasar ke fuskanta na matsanancin hali sakamakon janye tallafin man fetur ya haifar.

A ranar 2 ga watan Agustan da ya gabata ne dai kungiyoyin kwadago na NLC da TUC suka shirya zanga-zangar lumana a wasu daga cikin manyan biranen kasar domin nuna rashin amincewarsu kan matakin da gwamnatin shugaba Tinubu ta dauka na janye tallafin man fetur.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp