An zakuda shugabancin kamfanin mai na NNPC

Bayanan da ke fitowa daga kamfanin kula da man fetur na kasa NNPC na cewa an yi wa mafiyawan manyan daraktocin kamfanin ritaya daga aiki, duk da sauran watanni kusan 15 da suke da shi kafin wa'adin ritayarsu ya cika.

Wannan matakin kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, na zuwa ne kwanaki kadan bayan da kamfanin ya sanar da sallamar manyan mataimakan shugaban kamfanin su uku.

Daga cikin wadanda aka sallama, akwai Abdulkabir Ahmad da ke kula da bangaren iskar gas da Adokiye Tombomieye da ke kula da sashen albarkatun fetur.

A cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar da sanyin safiyar Talata, ya ce an dauki wannan matakin ne domin kara inganta aikinsa yadda zai zo daidai da zamani.

1 Comments

  1. Allah yasa wannan ya zama mafi Alkhairi ga yan'kasa baki Daya.

    ReplyDelete
Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp