Akwai fargabar yajin aikin NLC ba zai yi tasirin da ake bukata ba




Bankuna da hukumomin gwamnati da ke biyayya ga kungiyar kwadago ta NLC a Najeriya sun kauracewa guraren ayyukan su, yayin da yajin aikin ya doshi sa’o’I 24.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya NLC ya ruwaito cewa baki daya bankuna basu yi aiki a fadin kasar ba, yayin da wasu daga cikin ma’aikatun gwamnati suka fita aiki wasu kuma suka zauna a gida.

Tun farko dai kungiyar NLC ce ta kuduri aniyar tafiya yajin aikin na kwanaki biyu don nunawa gwamnatin kasar bacin ranta a game da rashin mayar da tallafin man fetur da ya haddasa tsadar rayuwa.

A cikin sanarwar da kungiyar ta fitar ta ce zata kuma tsunduma wani yajin aikin na sai baba ta gani nan da makonni biyu masu zuwa matukar gwamnati bata dauki matakin gyara bayan wannan yajin aikin da suka aiwatar ba.

DCL Hausa ta gano yadda mambobin na kungiyar NLC suka kulle kofofin shiga gidan talabijin din NTA na kasa da na Radio don hana ma’aikata shiga.

To amma dai masana a kasar na ganin zai yi wuya wannan yajin aikin yayi tasiri la’akari da barakar da ke tsakanin kungiyoyin kwadago guda biyu na NLC da TUC, kasancewar TUC ta barranta kanta da mambobin ta daga wannan yajin aiki.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp