NNPP ta kori jagora Kwankwaso


 

Jam’iyyar NNPP ta sanar da korar jagoranta Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso bayan da ta dakatar da shi makonni uku da suka gabata, sakamakon zargin sa da yiwa jam’iyyar zagon kasa tun bayan kammala babban zaben kasar.

Gidan rediyon Faransa, RFI Hausa, ya ce korar  ta Kwankwason na cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar dauke da sa hannun sakataren yada labaranta na kasa Abdulsalam Abdulrasaq.

Wannan dai na zuwa ne kasa da kwanaki uku bayan da wani tsagi na jam’iyyar ya sha alwashin gurfanar da tsohon gwamnan Kanon da wasu mabiyan sa a gaban shari’a, sakamakon zargin wadaka da fiye da naira biliyan 1 da aka tara a asusun jam’iyyar na kudaden sayar da fam din ‘yan Takara.

Sanarwar ta Abdulrasaq ta kuma kara da cewa korar kwanwason zata fara aiki ne nan take, yayin da yayi karin hasken cewa an dauki matakin ne bayan da Kwankwason ya ki bayyana a gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar, sakamakon gayyatar sa da aka yi don amsa wasu tambayoyi. 

Sakataren yada labaran jam’iyyar ya kuma tabbatar da cewa korar Rabi’u Kwankwaso na da goyon baya a cikin kundin jam’iyyar na shekarar 2022.

To sai dai da yake jam’iyyar ta rabu gida biyu kan matakin korar ta Kwankwaso, guda daga cikin masu goyon bayan sa kuma mai bincken kudi na jam’iyyar Ladipo Johnson yace bangaren da suka kori Kwankwason basu da alkibla kwata-kwata.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp