Wike ya umurci a kama wanda ya mallaki benen da ya rufta a Abuja

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya bayar da umurnin a jami'an tsaro su cafke mutumin da ya mallaki benen nan mai hawa biyu da ya ruguje a daren Laraba a unguwar Garki, Abuja.

Wike ya ba da umurnin a lokacin da ya ziyarci wurin da lamarin ya faru a ranar Alhamis.

ya kuma bukaci babban sakatare na hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja, Adesola Olusade, da ya biya kudaden jinyar wadanda ke kwance a asibiti.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp