Son Nijeriya ne ya sa muke son dawo da Bazoum a Nijar - Tinubu

https://drive.google.com/uc?export=view&id=11NV5sySC5phE0Zv-H9-LqJQE7ZbFOO6p
Shugaban Nijeriya kuma shugaban kungiyar ECOWAS Bola Tinubu ya ce shi da kansa ya gamsu yaki da kasar Nijar ka iya haifar da matsaloli ga yunkurinsa na samar kofofin arziki ga ‘Yan Nijeriya. Amma a cewarsa, kokarin da ECOWAS ke yi na dawo da Nijar cikin hayyacinta, yunkuri ne na kare muradu da martabar Nijeriya.

Tinubu ya fadi haka ne a yayin wata ganawa da ya yi a ranar Jumma’a da jakadan Amurka a Nijeriya. Shugaban na ECOWAS ya ce yana da matukar muhimmanci ECOWAS ta yi amfani da hanyoyin da suka wajaba wajen dawo da dimukuradiyya da hana sojojin tsawaita zamansu a Nijar .

Post a Comment

Previous Post Next Post