Sojojin da suka yi juyin mulkin Nijar sun bukaci dakarunsu su kasance cikin shirin kare kansu daga hare-haren da suke fargabar za su fuskanta.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce umurnin na kunshe a cikin wata takarda da majalisar koli ta mulkin sojin Nijar ta fitar a ranar Jumma’a. Sai dai kungiyar ECOWAS ta ce ba ta da niyyar afka wa Nijar, illa dai kokari take na mayar da Nijar din tafarkin dimukuradiyy ta hanyar diflomasiyya.
Category
Labarai