Sojojin Najeriya sun ceto karin dalibar Chibok

Rundunar sojin Najeriya karkashin Operation Hadin kai sun sanar da ceto karin dalibar Chibok guda daya.

 

Dalibar na cikin daliban Chibok 276 da ‘yan Boko Haram suka yi garkuwa da su a ranar 14 ga watan Afrilun 2014 a cikin makarantar su da ke kauyen Chibok na jihar Borno.

 

Da yake Karin haske kwamandan rundunar Manjo Janar Gold Chibuisi ya ce bayan likitoci sun kammala gwaje-gwaje akan dalibar mai suna Mary Nkeki, ya mikata ga hannun kwamishinan harkokin mata ta jihar Borno Hajiya Zuwaira Gambo. Dalibar mai shekaru 27 ta kubuta daga hannun Boko Haram din ne tare da mijinta wanda shi dan Boko Haram ne amma ya mika kai ga rundunar sojin mai suna Adamu. Bayanai sun nuna cewa sojojin sun yi nasarar gano Mary da mijinta ne akan iyakar Najeriya da Kamaru a kokarin da suke yi na guduwa daga sansanin ‚yan Boko Haram din, bayan da mijinta ya kuduri aniyar ajiye makamin sa. Kafofin yada labaran Najeriya sun ruwaito cewa Mary ta haifi yara guda biyu, sai dai sun mutu a sakamakon matsanaciyar cutar yunwa da ta kama su lokacin da suke cikin dajin Gulumba dake karamar hukumar Bama ta jihar Borno.

 


 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp