Burkina Faso ta taimakawa Nijar da motoci 300 na kayan abinci

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa manyan motocin daukar kaya fiye da 300 daga Burkina Faso sun isa birnin Niamey a kokarin da kasar ke yi na ragewa yan Nijar radadin takunkuman da aka Sanya musu. 

Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da kasashen Benin da Najeriya manyan kasashen da ake shigar da abinci jamhuriyar Nijar suka rufe iyakar su da kasar wadda ke karkashin juyin Mulki.

Tun bayan juyin mulkin na Nijar ta ke samun goyon bayan gwamnatin kasashen Burkina Faso da Mali, abinda masana ke ganin hakan yana da alaka da kasasancewar su sojoji.

Bayanai sun ce motocin makare da kayan abincin sun sami rakiyar sojojin Burkina Faso, kafin daga bisani suka mikasu hannun sojojin Nijar akan iyakar kasashen biyu.

Ko da yake jawabi daraktan hukumar hana fasa kwauri ta jamhuriyar Nijar Kanal Adamou Zaraoumeye yace hukumar sa ta karbi motoci guda 300 makare da kayan abinci da suka hadar da masara da gishiri da sauran kayan masarufi.

A cewar sa nan ba da jimawa ba za’a far araba ayan ga jama’ar kasar da nufin rage musu radadi.

 


 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp