Shugaba Tinubu ya umurci a rufe duk wata kan iyaka da Nijeriya ta yi da Jamhuriyar Nijar



Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya umurci da a rufe dukkanin iyakokin da Nijeriya ta yi da Jamhuriyar Nijar.

Sabon shugaban hukumar kwastam na kasa Adewale Bashir Adeniyi ya sanar da hakan a lokacin da ya ziyarci kan iyakar Magamar Jibia, jihar Katsina.

Ya ce shugaban kasa ya umurci da a rufe dukkanin iyakokin har sai baba-ta-gani ta dalilin hambarar da gwamnatin Bazoum da sojoji suka yi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp