Ba Turawan Yamma ke ingiza mu daukar mataki kan Nijar ba - ECOWAS

Kungiyar ECOWAS ya musanta rade-radin da ake yi cewa Turawan Yamma ne ke juya akalarta game da rikicin juyin mulkin Nijar.

Shugaban hukumar kungiyar ta ECOWAS Omar Aleiu Touray ne ya sanar da hakan a Abuja a lokacin da ya kira taron manema labarai.

A ranar 26 ga Julin 2023 ne dai sojoji suka hambarar da gwamnatin farar hula ta Bazoum a Nijar, inda sojojin suka nada Janar Abdourahamane Tchiani a matsayin shugaba na riko.

Kungiyar ECOWAS dai ta sha sukar lamirin sojojin da suka yi wannan juyin mulkin, inda suka saka wa Nijar dokoki daban-daban da zummar sojojin su ji matsi su mayar da gwamnatin farar hula a kasar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp