Karamin ministan man fetur Heineken Lokpobiri ya ce matatar man fetur ta Port Harcourt za ta dawo aiki a cikin watan Disambar bana.
Ministan ya ba da wannan tabbacin ne a yayin wani rangadin duba ci gaba da aikin gyaran da ake yi a matatar man ta garin Fatakwal na jihar Ribas a ranar Juma’ar nan.
Ya kuma ce gwamnatin tarayya za ta fara gyaran matatar Warri a watannin uku farko na shekara mai zuwa, sannan kuma za a gyara ta Kaduna cikin karshen shekara mai zuwa.