Gwamnatin Nijeriya ta sanar da lokacin da matatun man kasar za su dawo aiki

Karamin ministan man fetur Heineken Lokpobiri ya ce matatar man fetur ta Port Harcourt za ta dawo aiki a cikin watan Disambar bana.

Ministan ya ba da wannan tabbacin ne a yayin wani rangadin duba ci gaba da aikin gyaran da ake yi a matatar man ta garin Fatakwal na jihar Ribas a ranar Juma’ar nan.

Ya kuma ce gwamnatin tarayya za ta fara gyaran matatar Warri a watannin uku farko na shekara mai zuwa, sannan kuma za a gyara ta Kaduna cikin karshen shekara mai zuwa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp