Rashin sanin tarihi zai sa ku tabka kuskure irin na magabata - Atiku


 

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya jaddada muhimmancin ilimin tarihi wajen gina kasa. Maitamaki na musamman kan harkokin yada labarai ga Atikun ya ce Waizrin Adamawa ya ambata hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin ayarin hukumar editocin jaridar The Sun karkashin babban editan ta Mr. Onuoha Ukeh yayin da suka kai masa ziyara a gidan sa da ke Abuja a wannan Talata.

 Tsohon mataimakin shugaban kasar Wanda yanzu haka ke kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasa a gaban kotu, kasancewar sa wanda ya yiwa jam'iyyar PDP takara, ya ce ba tare da la'akari da darrusan da tarihi ya nuna ba, za a ci gaba da maimaita kura-kuran da aka tafka a baya. Yace wadanda suke zaune ba tare da sanin abin da ya gabace su ba, akwai yuwuwar su aikata kura-kuran magabata, inda ya ce ba daidai ba ne a cire darasin tarihi daga manhajar koyarwar makarantun Nijeriya.



Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp