Mata ta kai mijinta kara kotu saboda ya shekara 2 ba su yi saduwar aure ba


Wata matar aure mai kimanin shekaru 25 mai suna Ruqayya Mukhtar a ranar Alhamis din nan ta shaida wa wata kotun shari’a da ke zamanta a unguwar Rigasa da ke jihar Kaduna cewa mijinta ya shafe shekara biyu bai kwanta da ita ba.

Matar wadda ta shigar da kara ta roki kotu da ta raba aurenta da mijinta mai suna Naziru Hamza, ta kuma koka kan yadda mijin ke cin zarafinta.

Sai da mijin ya musanta dukkanin zarge-zargen da ake yi masa inda ya ce yana yin iya bakin kokarinsa wajen ganin ya gamsar da matarsa a yayin saduwa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp