Mahaukacin kare ya hallaka jaririya 'yar watanni biyar tana goye bayan mahaifiyarta

Wani mahaukacin kare a birnin Osogbo na jihar Osun  ya yi sanadiyyar mutuwar wata jaririya 'yar watanni biyar da haihuwa.

Mahaifiyar jinjirar Nafisat Muideen ta ce lokacin da lamarin ya faru a cikin rukunin gidajen Hallelujah babu wadanda za su kai mata daukin gaggawa.

Mahaifiyar jinjirar ta ce lamarin ya faru da misalin karfe 1:45 na rana a lokacin da take kan hanyar zuwa shago don sayo wa diyar magani.

Ta ce tana cikin tafiya ta ji haushin kare a bayanta, juyawarta ke da wuya, karen ya yi tsalle ya cimma yarinyar da ke goye a bayanta.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp