Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya sanar da rage kudin rajistar shiga manyan makarantun jihar, a wani mataki na rage tsadar rayuwar da ke addabar jama'a ciki har da Kaduna. Sanarwar da DCL Hausa ta samu a kan wannan batu ta nuna cewa yanzu kudaden rajistar makaratun jihar sun koma kamar haka:
Jami'ar Jihar Kaduna
- Kudin makarantar sun koma 105,000 a maimakon N150,000
Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli
- Kudin makarantar sun koma N50,000 a maimakon N100,000
Kwalejin Kiwon Lafiya ta Shehu Idris Makarfi
-HND: N70,000 a maimakon N100,000
-ND: 52,000 a maimakon N75,000
Wannan na zuwa ne a kwanaki kalilan bayan da wasu mata a jihar ta Kaduna suka yi zanga-zangar tsadar rayuwa.
Category
Labarai