Mutuwar fuju’a ta firgita dalibai a Enugu


 Ana ci gaba da zaman dar-dar yayin da rudani ya mamaye zukatan dalibai da mazauna kewayen jami’ar kimiyya da Fasaha ta jihar Enugu bayan da wasu dalibai har 13 suka mutu sakamakon wata cuta da ba’a santa ba cikin ‘yan makonni.

 

Wasu daga cikin daliban jami’ar sun shaidawa jaridar Premium Times cewa abokan karatun su 13 ne suka mutu cikin kasa da makonni 2 sakamakon wata cuta mai ban tsoro da basu santa ba.

A cewar daliban cikin 13 da suka mutu guda daya ce kadai aka yi gaggawar kaita asibitin koyarwa na jihar Enugu, inda ta cika a can, kuma har yanzu ba’a gaya musu dalilin mutuwar ta ba.

Daliban sun kuma kara da cewa da zarar dalibi ya fara nuna alamun rashin lafiya zai mutu nan take ba tare da bata lokaci ba, abinda ke kara jefa su cikin razani.

Ko da ta ke karin haske kungiyar dalibai ta NANS reshen kudu maso gabashin Najeriya ta bukaci mahukuntan makarantar su yi gaggawar rufe ta don ceto rayukan sauran dalibai.

Ta cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar na shiyyar Kudu maso gabas Chidi Nzekwe ya fitar, ya ce kungiyar ta damu matuka da irin wannan mutuwa mai ban mamaki, don haka akwai bukatar mahukunta su yi gaggawar daukar mataki don gano dalili.

Sai dai kuma a wani martanin gaggawa da shugaban sashen kula da dalibai na jami’ar Jude Udenta ya yi ta cikin sanarwar da ya fitar, ya yi watsi da bukatar kungiyar dalibai na rufe makarantar.

Ta cikin sanarwar, Mr Udenta ya musanta labarin cewa dalibai 13 ne suka mutu, yana mai cewa dalibai 5 ne kachal suka mutu, yayin da yace guda daga cikin su ya mutu ne a sakamakon hadarin mashin, kuma shi kadai ne ya mutu a cikin makaranta.

“Mu kan mu muna cikin rudani, kuma muna mamakin irin wannan mutuwa, amma batun mutane 13 sun mutu ba haka bane, tun farko mu bamu so maganar ta fita bainar jama’a ba, saboda a ganin mu bai dace ana yamadidi da mutuwar daliban mu ababen kaunar mu a duniya ba” in ji Mr Udenta.

Mr Udenta ya kuma kara da cewa sauran dalibai hudun da suka mutu sun mutu ne a wajen jami’ar, don haka babu tabbas game da dalilin mutuwar su, ikirarin da tuni daliban suka musanta, bayan da suka tabbatarwa manema labarai cewa dukannin dalibai 13 sun mutu a dakunan kwanan dalibai wasu kuma a cikin aji.

Wannan labari mai cike da sarkakiya dai tuni ya tilastawa gwamnatin Jihar kafa kwamitin bincike karkashin jagorancin sakataren gwamnatin Jihar Chidiebere Oniya.

Yayin ziyarar da kwamitin ya kai jami’ar Mr Oniya ya ce, baya ga binciken, gwamnatin jihar ta kuma umarci kwamishinan harkokin lafiya Emmanuel Obi da ya gudanar da nasa binciken daban kan yanayin tsafta, lafiya da ma yanayin da karamin asibitin shaka ka tafi na jami’ar ke ciki, saboda irin muhimmancin da daliban jami’ar ke da shi ga jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp