Abuja ba wajen kiwon shanu ba ne - Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT) Nyesom Wike ya sha alwashin kawo karshen kiwon shanu a cikin birnin Abuja.

Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da ya kira sa’o’i kadan bayan an rantsar da shi a matsayin ministan na Abuja ranar Litinin.

“Za mu tuntubi makiyaya cikin laluma domin mu ga yadda za su daina (kiwo a fili) saboda ba za mu iya barin shanu a cikin gari ba,” in ji shi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp