Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT) Nyesom Wike ya sha alwashin kawo karshen kiwon shanu a cikin birnin Abuja.
Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da ya kira sa’o’i kadan bayan an rantsar da shi a matsayin ministan na Abuja ranar Litinin.
“Za mu tuntubi makiyaya cikin laluma domin mu ga yadda za su daina (kiwo a fili) saboda ba za mu iya barin shanu a cikin gari ba,” in ji shi.