Kishi: Magidanci ya saki matarsa bayan likita namiji ya karbi haihuwar da za ta yi a Katsina

Magidanci a jihar Katsina ya saki matarsa da suka shafe shekaru 14 da aure saboda an bar wani likita namiji ya karbi haihuwar da matar za ta yi a wani asibiti.

Babbar Darakta ta kungiyar kula da mata da yammata Nana Women and Girls Initiative, Dr Fatima Adamu, ta bayyana hakan a ranar Alhamis.

A cewarta matar wadda mijinta ya sake ta, an ce ta samu matsala mai sarkakiya yayin nakuda wanda hakan ya sa aka garzaya da ita asibiti inda babu wata likita mace a bakin aiki da za ta duba ta.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp