Daliban wata makarantar Sakandare sun zane malaminsu

Wasu daliban makarantar sakandire su goma a jihar Ogun sun lakada wa wani malaminsu, Kolawole Shonuga dukan tsiya saboda ya hana daya daga cikinsu satar amsa a lokacin da suke rubuta jarabawa.

Majiyar DCLHausa ta jaridar PUNCH ta ce lamarin ya faru ne a ranar Talatar da ta gabata a makarantar Isanbi Comprehensive High School da ke Ilisan-Remo a karamar hukumar Ikenne a jihar.

A cewar jaridar malamin mai suna Shonuga, a yayin da yake tsaron jarabawar a ajin daliban SS 1, ya kama wani matashi mai suna Ashimi Adebanjo mai shekaru 18 da haihuwa, yana satar amsa inda nan take ya kwace takardarsa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp