Ganduje zai mika wa Abba mulkin Kano a Lahadi maimakon Litinin


Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje zai mika wa sabon gwamna Abba Kabir Yusuf mulkin jihar Kano tun wannan Lahadi da misalin karfe 9pm a maimakon Litinin 29.05.2023 da aka tsara mika mulkin. 

Rahotannin da DCL HAUSA ta samu sun ce Ganduje zai yi haka ne domin ba shi damar halartar bikin rantsuwar kama aiki na Bola Ahmed Tinubu, wanda za a rantsar shi ma a Litinin din nan a matsayin shugaban Nijeriya na 16.

To amma duk da haka rahotanni sun ce zababben gwamnan Kanon zai yi bikin shan ruwarsa a Litinin kamar yadda aka tsara.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp