Mutane 25 ne suka rasa rayukansu, yayinda da 53 suka jikkata a wani hadarin mota a Kano
Hukumar kiyaye afkuwar haddura ta kasa reshen jihar Kano, ta tabbatar da mutuwar matafiya 25, yayin da wasu 53 suka samu raunuka a wani hatsarin mota.
Hatsarin ya afku ne da sanyin safiyar Litinin a kusa da Kasuwar Dangwaro, dake hanyar zariya a Kano.
Matafiyan sun yi lodi ne a cikin wata tirela wadda take dauke da shanu ta da zata tafi yankin kudancin Nijeriya daga Maiduguri.
A cewar kwamandan hukumar FRSC a jihar, Ibrahim Abdullahi, hatsarin ya afku ne da wata tirela (IVECO) mai lamba XA 311 ZB.
Yace an kira su ne da misalin karfe 03:15 na daren ranar 1 ga Yuli, 2024. Da samun labarin, suka yi gaggawar aika jami’ai da motar zuwa inda lamarin ya faru domin ceto wadanda lamarin ya shafa da karfe 03:30.
Kwamandan sashin ya ce hatsarin ya afku ne sakamakon gudun wuce gona da iri da motocin keyi.