Likitoci za su tsunduma yajin aiki a jihar Kano.

 Likitoci za su tsunduma yajin aiki a jihar Kano.





Kungiyar likitocin hakori ta kasa (NAGGMDP) reshen jihar Kano ta bayyana shirin fara yajin aikin gargadi na tsawon mako biyu domin nuna rashin amincewa da wasu matsaloli da su ka dabaibaye tsarin kiwon lafiyar jihar.


A cikin sanarwar da shugaban kungiyar, Dr Aminu Kabir Muhammad ya sanya wa hannu a ranar Laraba, kungiyar ta bayyana cewa za a fara yajin aikin a asibitocin fadin jihar daga karfe 12:00 na safe ranar 17 ga watan Yuni 2024.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp