Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya maka hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC kotu domin hana kama shi.
An gabatar da karar da aka shigar a babbar kotun Kano a gaban mai shari’a Yusuf Ubale.
Wata majiya ta bayyana cewa karar na da nufin hana hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC tsare shi.
Allah kasa mu d@che
ReplyDelete