Kwankwaso ya maka EFCC a kotu

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya maka hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC kotu domin hana kama shi.

An gabatar da karar da aka shigar a babbar kotun Kano a gaban mai shari’a Yusuf Ubale.

Wata majiya ta bayyana cewa karar na da nufin hana hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC tsare shi.

Idan dai za a iya tunawa, EFCC na binciken zargin da ake yi wa Kwankwaso kan kudi naira biliyan 2.5 na kudaden yakin neman zabe da ke da alaka da jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a kan Kwankwaso.

1 Comments

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp