Ba ni da alaka da fastocin da ake likawa ni da El-Rufai a Kaduna - Akpabio


Ba ni da alaka da fastocin da ake likawa ni da El-Rufai a Kaduna - Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriaya, Godswill Akpabio, ya musanta cewa yana da hannu a yada fastoci a jihar Kaduna da ke nuna kawancen siyasa da tsohon Gwamna Nasir El-Rufai a zaben shugaban kasa na shekarar 2027.

Hakan na a cikin wata sanarwa da mai ba Shugaban Majalisar Godswill Akpabio shawara kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Eseme Eyiboh ya fitar a ranar Laraba yana mai cewa yada fastocin aikin wasu mutanene da basa sun zaman lafiya.

Eyiboh ya ce Akpabio ba shi da niyar neman tikitin tsayawa takarar shugaban kasa shida El-rufai a shekarar 2027.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp