Za a fara jigilar maniyyatan jihar Kano ranar Juma’a mai zuwa


Babban darakta a Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Baba Danbappa, ya ce za a fara jigilar maniyyatan jihar ranar Juma’a 24 ga watan Mayu, 2024.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da aka naɗa mataimakin Gwamnan jihar Kano, Commarade Aminu Abdussalam Gearzo a matsayin Amirul Hajj.

Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ne ya sanar da hakan yayin wani shiri na aikin hajji da aka gudanar a sansanin Alhazai yau Litinin.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp