Majalissar wakilai ta Nijeriya ta umurci babban bankin kasar CBN da ya janye batun cajin kaso biyar a hahadar tura kudade a bankunan kasar nan

 Majalissar wakilai ta Nijeriya ta umurci babban bankin kasar CBN da ya janye batun cajin kaso biyar a hahadar tura kudade a bankunan kasar nan.

Majalisar wakilai ta umarci babban bankin Nijeriya (CBN) da ya janye takardar da ta umarci bankunan kasuwanci da su fara cire harajin da ake sakawa ta yanar gizo kan duk wata hada-hadar kasuwanci da ‘yan Nijeriya ke yi.


Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da jama'a ke nuna rashin jin dadinsu kan wannan harajin da kungiyoyin kwadago da kungiyoyin kwararru da dama na kasuwanci da kuma daidaikun mutane ke yi.


‘Yan majalisar sun ce babban bankin ya yi wa tanadin dokar mummunar fassara, don haka ya kamata a gaggauta sake fitar da wata takardar domin wannan bata dace ba kamar yadda doka ta tanada.


Harajin 0.5% akan duk ma'amala ta banki, bisa ga Sashe na 44 na Dokar Canza Laifukan Intanet, 2024, ana sa ran 'yan kasuwa da masu kula da harkokin kasuwanci da Dokar don ba da gudummawar Tsaro ta Intanet ta Kasa, Asusun zai kasance a cikin CBN, kuma ofishin mai ba da shawara kan harkokin tsaro (ONSA) ne ke gudanar da shi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp