Babu dalilin da zai sa Nijeriya ta dogara da shigo da abinci daga wasu kashashe-Inuwa Yahya

Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce da yawan filayen noma da yawan al’umma, Nijeriya ba ta da dalilin dogaro da shigo da abinci daga kasashen waje.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a wajen kaddamar da wani kamfanin taki da sinadarai a jihar.

Gwamnan wanda ya bayyana kudurin gwamnatinsa na ci gaba da bunkasa harkar noma a jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan  Ismaila Uba Misilli ya fitar, gwamnan ya ce,  za su ci gaba da bunkasa harkar noma a Gombe ta hanyar tallafa wa wadannan masana’antu.


Yace gwamnatin su ta himmatu 100% don bunkasa noma, babbar ma’aikata ta jiha da kasa. Kuma tun lokacin da m su ka hau kan karagar mulki a shekarar 2019, samar da abinci ya zama babban abin da ya fi mayar da hankali a gare su.


Babu dalilin da zai sa Nijeriya ta dogara da shigo da abinci daga wasu kasashe dole a jajirce wajen noma abinda za aci a kasa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp