Jami'an tsaron Nijeriya sun kubutar da 'ya'yan da majalisar Zamfara da aka sace bayan watanni 17.

Jami'an tsaron Nijeriya sun kubutar da 'ya'yan da majalisar Zamfara da aka sace bayan watanni 17.


Ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (ONSA) da ‘yan sanda sun ceto ‘ya’yan dan majalisar dokokin jihar Zamfara, Aminu Ardo bayan shafe watanni 17 a hannunsu.


Mataimakin jami’in hulda da jama’a na rundunar, CSP Isuku Victor, a lokacin da yake mika ‘yan matan ga mahaifinsu, ya ce, mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ne ya dauki nauyin ceto ‘yan matan, tare da hadin gwiwar jami’an tsaro.


A watan Nuwambar shekarar 2022,ne wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kai farmaki gidan Aminu Ardo da ke Jangebe, Jihar Zamfara, inda suka yi garkuwa da matarsa da ‘ya’yansa guda hudu.


Mahaifiyar da wasu yaran biyu sun yi nasarar tserewa a lokacin da aka yi garkuwa da su, inda suka bar Maryam da Nana Asma’u tare da wadanda suka yi garkuwa da su.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp