Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya nada mukaddashin shugaban Gidan Talabijin na ARTV.

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya nada mukaddashin shugaban Gidan Talabijin na ARTV.

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin Hajiya Hauwa Isa Ibrahim a matsayin mukaddashin darakta na gidan talabijin na Abubakar Rimi (ARTV).


SolaceBase ta ruwaito cewa nadin ya biyo bayan dakatarwar da aka yi wa manajan daraktan gidan Mustapha Indabawa.


Wasikar mai dauke da sa hannun Abdullahi Baffa Bichi, sakataren gwamnatin jihar Kano tare da kwanan watan 27 ga watan mayu 2024,

wasikar ta umurce ta da ta karbe harkokin gidan talabijin da radiyon nan take.


Har zuwa nadin nata, Hajiya Hauwa Isa Ibrahim ita ce mataimakiyar darakta a gidan talabijin na Abubakar Rimi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp