Cutar kyanda tayi sanadiyyar mutuwar su yara 49 a jihar Adamawa.

Cutar kyanda tayi sanadiyyar mutuwar su yara 49 a jihar Adamawa.

Adadin wadanda suka rasa rayukan su sakamakon kamuwa da cutar kyanda a jihar Adamawa ya kai 49.


Hakan ya fito ne a daidai lokacin da jami’an gwamnatin jihar ke bayar da bayanai kan kokarin dakile cutar yayin da hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta yi jawabi ga manema labarai a birnin Yola kan ka’idojin bayar da rahoto na gaskiya kan cutar.


A yayin taron wayar da kai na WHO a ofishin ta na Yola, masanin cutar kanjamau na jihar Adamawa, Kadabiyu Jones, ya ce kawo yanzu an samu rahoton mutuwar mutane 49, yayin da 143 daga cikin 818 da ake zargin sun kamu da cutar kyanda ya tabbatar da sun kamu da cutar.


Ya ce wadanda abin ya shafa yara ne da ke tsakanin shekara 1 zuwa 14, kuma yawancinsu ba a taba yi musu allurar riga-kafi ba.


Ya tabbatar da cewa jihar ta tura jami’an sa ido domin gano bullar cutar kuma tana aiki tukuru don ganin kawo karshen kamuwa da cutar ta hanyar rigakafin da ake yi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp