Tinubu ya sanya hannu kan kudirin dokar bawa dalibai rancen kudin karatu.

 Tinubu ya sanya hannu kan kudirin dokar bawa dalibai rancen kudin karatu.


Shugaban kasa Bola Tinubu, ya sanya hannu kan kudurin lamuni ga daliban Nijeriya ya zama doka.

Hakan na zuwa ne bayan nazari da majalisar dattawa da ta wakilai suka yi na rahoton kwamitin kula da manyan makarantu da TETFUND ya gudanar.

Da yake jawabi bayan ya sanya hannu kan kudirin dokar, Tinubu ya ce babu wani dan Nijeriya ko wanene da za a cire daga cikin tsarin samar da ingantaccen ilimi.


Yace gwamnatinsu ta kuduri aniyar ganin an baiwa ilimi kulawar da ta dace, gami da shirye-shiryen bunkasa fasaha ta fannoni da dama.

an fito da wannan shiri ne domin tabbatar da cewa babu wani wanda komai talaucinsa da za a cire shi daga cin gajiyar wannan shiri,domin gina makomar matasan Nijeriya kamar yadda shugaban ya bayyana a fadarsa dake Villa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp