An samu wata fashewa cikin wani barikin sojoji da ke Lagos


 


Rundunar sojin Nijeriya ta tabbatar da fashewar wani abu a barikinta da ke Ikeja a Lagos. Lamarin ya haifar da rudani ga mazauna barikin. 

Amma a sanarwar da mai magana da yawun rundunar soji ta kasa Manjo Janar Onyema Nwachukwu ta ce fashewar ba wata mai girma ba ce. 

Ya ce an samu hakan ne a wata gona da ke kusa da kasuwar Mammy da ke barikin na Ikeja, inda ake zargin wasu abubuwa da wani manomi ya binne a cikin gona suka haddasa fashewar.

Post a Comment

Previous Post Next Post