Gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da kafa dokar takaita zirga-zirga a kan iyakar jihar da jihohin Sokoto da Katsina da misalin 7 na yamma zuwa 6 na safiya.
Kwamishinan yada labaran jihar Munir Haidara ya sanar da hakan ga manema labarai a Gusau, inda ya ce an dauki matakin ne don kara dakile ayyukan ta'addanci a jihar.