Hadaddiyar Daular Larabawa ta ce za ta dawo da bayar da biza ga 'yan Najeriya, hakan wani mataki ne na karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.
Bayanin hakan na a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar a yau Talata.
Wannan dai na zuwa ne shekaru biyu bayan da Daular Larabawa ta sanya wa yan Najeriya takunkumin shiga kasar.
A cewar hukumomin Hadaddiyar Daular Larabawar an dawo da shirin ya fara aiki ne daga ranar 4 ga watan Maris din shekarar 2024, wanda hakan ya samo asali ne sakamakon tattaunawa tsakanin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na UAE, Sheikh Mohamed bin Zayad Al Nahyan.